Isa ga babban shafi
Nijar

Boko Haram ta kashe dakarun Nijar 10

Rahotanni daga jamhuriyar Nijar sun tabbatar da mutuwar dakarun kasar 10 yayin da wasu 4 suka bata, sakamakon wani harin kwonton-bauna da mayakan Boko Haram suka kai masu a cikin daren Asabar zuwa wayewar garin jiya lahadi.

Wasu daga cikin dakarun Nijar da ke yaki da Boko Haram
Wasu daga cikin dakarun Nijar da ke yaki da Boko Haram Reuters
Talla

Ma’aikatar tsaron kasar ta ce, lamarin ya faru ne a wani wuri da ke cikin jihar Diffa kusa da yankin tafkin Chadi, kuma kafin su arce, maharan sun kona motocin soji akalla uku.

A cikin watan Afrilun da ya gabata ne, gwamnatin Nijar ta sanar da kaddamar da wani aikin soji da zimmar kakkabe mayakan Boko Haram a yankin tafkin Chadi da ya hada kasashen Nijar da Chadi da Najeriya da kuma Kamaru.

A bangare guda, a yau Litinin ake fara shara’ar mutanen da ake zargin cewa mayakan Boko Haram ne a garin na Diffa, karo na farko, duk da cewa kawo yanzu ba a san adadin wadanda za su gurfana a gaban kotun ta musamman ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.