Isa ga babban shafi
Nijar

Mataimakiyar sakataren MDD na ziyara a Nijar

Amina Muhammad, mataimakiyar sakataren majalisar dinkin Duniya na ziyara a Jamhuriyar Nijar, inda a yau ta ziyarci Jihar Maradi don gani da ido, kan irin ayyukan da hukumomin Majalisar ke yi keyi kan hakkokin yara, ilimin mata, kiwon lafiya, da kananan sana’o’in mata sannan da batun canjin yanayi.

Amina Muhammad, mataimakiyar sakataren majalisar dinkin duniya yayin da ta isa Jamhuriyar Nijar
Amina Muhammad, mataimakiyar sakataren majalisar dinkin duniya yayin da ta isa Jamhuriyar Nijar RFIHAUSA
Talla

A ranar Asabar 7 ga watan Yuly na shekarar 2018, mataimakiyar sakataren majalisar dinkin duniyar ta soma ziyarar a Jamhuriyar Nijar.

A cewar Amina Muhammad babban makasudin ziyarar shi ne karfafa samar da hakkokin mata a fannonin Ilimi, Lafiya da kuma basu damar shiga al’amuran siyasa wajen tafiyar da al’amuran mulkin kasa.

Wakilinmu daga Maradi Salisu Isa ya aiko mana da Rahoto.

01:41

Mataimakiyar sakataren MDD na ziyara a Nijar

Salisu Isah

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.