Mataimakiyar sakataren MDD na ziyara a Nijar
Amina Muhammad, mataimakiyar sakataren majalisar dinkin Duniya na ziyara a Jamhuriyar Nijar, inda a yau ta ziyarci Jihar Maradi don gani da ido, kan irin ayyukan da hukumomin Majalisar ke yi keyi kan hakkokin yara, ilimin mata, kiwon lafiya, da kananan sana’o’in mata sannan da batun canjin yanayi.
Wallafawa ranar:
A ranar Asabar 7 ga watan Yuly na shekarar 2018, mataimakiyar sakataren majalisar dinkin duniyar ta soma ziyarar a Jamhuriyar Nijar.
A cewar Amina Muhammad babban makasudin ziyarar shi ne karfafa samar da hakkokin mata a fannonin Ilimi, Lafiya da kuma basu damar shiga al’amuran siyasa wajen tafiyar da al’amuran mulkin kasa.
Wakilinmu daga Maradi Salisu Isa ya aiko mana da Rahoto.
Mataimakiyar sakataren MDD na ziyara a Nijar
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu