Isa ga babban shafi
Nijar

Nijar ta janye dokar haramta sana'o'i a Diffa

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta cire dokar da ke hana kamun kifi, noman tattasai da sauran amfanin gona a zagayen kogin Komadugu a jihar Diffa, dokar da aka kafa bisa zargin cewa ‘yan Boko Haram na amfani da wadannan sana’o’i don samun kudade tsawon shekaru hudu da suka gabata.

Kofar garin Diffa da ke kan iyaka da Najeriya mai fama da rikicin Boko Haram
Kofar garin Diffa da ke kan iyaka da Najeriya mai fama da rikicin Boko Haram AFP PHOTO / PIUS UTOMI EKPEI
Talla

Wata majiya a ma’aaikatar cikin gidan kasar ta Nijar, ta ce an cire dokar ne lura da yadda ake kara samun zaman lafiya a yankin da ke gaf da iyakar Nijar da Najeriya.

Wata kungiyar agaji mai zaman kanta OXFAM, ta ce a kowace shekara manoman yankin na samun sama da Euro milyan 42 sakamakon noman tattasai da kuma kamun kifin a yankin.

Sai dai tattalin arzikin yankin ya gamu da gagarumar matsala saboda dokar haramcin sana’o’in, lamarin da ya jefa dubban jama’a cikin talauci a yankin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.