Dandalin Siyasa
Shirin Dandalin Siyasa, yana tattaunawa tare da tafka muhawar kan al’amurran siyasa da ke faruwa a kasashen duniya, da batutuwan da suka shafi al’umma kai tsaye, wanda Bashir Ibrahim Idris ke jagoranta. Wannan Shirin na zuwa ne a karshen mako Ranar Assabar da maimaci a ranar Lahadi a Shirye Shiryen Safe da Yamma.
Ci gaban karatuSaurari kashin karshe
Daukacin kashi-kashi
-
Majalisar Najeriya ta gayyaci Buhari don yi mata bayani kan tsaro
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya yi nazari kan kiran da Majalisar Tarayyar Najeriya ta yi shugaba Muhammadu Buhari don yi mata bayani kan tabarbarewar tsaro a kasar.08/05/201910:12 -
Rikicin shugabancin Majalisar Wakilai a Najeriya
Shirin dandalin siyasa a wannan makon ya sake yin duba kan dambarwar neman shugabancin Majalisar Najeriyar karo na 9 da sabbin zababbun 'yan Majalisar wakilan kasar ke tafkawa. A yi sauraro lafiya.17/04/201910:27 -
Dambarwar Jam'iyyar APC kan shugabancin Majalisun Najeriya
Har yanzu Jam'iyyar APC ta gaza shawo kan matsalolinta da suka shafi 'yan majalisun da za su jagoranci majalisar Dattijai da ta wakilai, dai dai lokacin da ake ci gaba da fuskantar rarrabuwar kai.10/04/201911:11 -
Fatan yan Najeriya dangane da sabuwar Majalisa bayan zabe
Bayan wata daya da kawo karshen zaben Shugaban kasa da na wasu yan majalisu a Najeriya,hankulan yan kasar da dama ya koma zuwa zauren Majalisa .Haka zalika wasu daga cikin yan majalisun da suka samu goyan bayan jama'a sun sheidawa Bashir Ibrahin Idris a cikin shirin Siyasa fatan su da kuma irinn rawar da za su iya takawa a Majalisa don kawo sauyi a siyasar kasar,banda haka wasu sun bayyana damuwa a kai.03/04/201910:58 -
Dambarwar zabukan Najeriya na 2019
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ne kan dambarwar zabukan Najeriya, in da Jam'iyyar adawa ta PDP ta garzaya kotu domin kalubalantar nasarar shugaba Muhammadu Buhari na APC a zaben 2019, yayinda ita ma APC a jihar Bauchi ta ruga zuwa kotu duk dai akan batun na zabe.20/03/201910:45 -
Nazari kan zaben Gwamnoni a Najeriya
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya yi nazari ne game da zabukan Gwamnoni na 'yan majalisun jihohin Najeriya da za a gudanar a ranar Asabar mai zuwa, in da ake fargabar cewa, da dama daga cikin Gwamnoni masu ci ba za su koma kan kujerunsu ba saboda wasu dalilai na siyasa.07/03/201909:57 -
Shugaba Buhari ya lashe zaben Najeriya wa'adi na biyu
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ne game da nasarar da shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya samu ta sake lashe kujerar shugabancin kasar wa'adi na biyu bayan doke babban abokin hamayyarsa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar. Tuni Jam'iyyar PDP ta bayyana sakamakon zaben a matsayin mara inganci tana mai zargin tafka magudi a zaben,yayinda ta ce, za ta shigar da kara a kotu.28/02/201911:01 -
2019: Hankulan kasashen duniya sun karkata zuwa zabukan Najeriya
Shirin Dandalin Siyasa na wannan mako da Bashir Ibrahim Idris ya gabatar, yayi nazari kan halin da siyasar Najeriya ke ciki, yayinda ya rage kwanaki kalilan a gudanar da zabukan kasar na 2019 a matakai daban daban. Sai kuma tsokaci da shirin ya yi kan yadda hankulan kasashen duniya ya karkata zuwa kan zabukan Najeriyar.13/02/201910:37 -
Yadda Siyasa ke gudana a Jihar Kano gabanin zaben shugaban kasa
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon, ya leka jihar Kano da ke tarayyar Najeriya, ida yayi nazari kan yadda al'amuran Siyasa ke gudana, yayinda ake gaf kada kuri'a a zaben shugabancin kasar na 2019 a ranar 16 ga watan Fabarairu.08/02/201910:20 -
Dambarwar siyasar dakatar da Onnoghen
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ne kan dambarwar siyasar da ta kunno kai a Najeriya bayan shugaban kasar Muhammadu Buhari ya dakatar da alkalin alkalai, Walter Onnoghen bisa zargin sa da bayar da bayanan karya kan kudaden da ya mallaka.31/01/201910:40 -
Shiri kan dakatar da Babban mai shari'ar Najeriya
Shirin Dandalin siyasa na wannan mako ya mayar da hankaline kan dakatar da babban mai shari'ar Najeriya Walter Onnonghen da Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari yayi.30/01/201910:40 -
'Yan siyasa na sauya sheka a Najeriya
Shirin Dandalin Siyasa na wannan makon tare da Bashir Ibrahim Idris ya tattauna ne kan yadda 'yan siyasa ke ci gaba da sauya sheka a Najeriya a daidai lokacin da ake shirin gudanar da zaben gama-gari a cikin watan gobe.17/01/201910:33 -
Kun san abin da Buhari ya fada a Akwa Ibom?
Shugaban Najeriya Muhammdu Buhari da ya kaddamar da yakin neman zabensa a jihar Akwa Ibom, ya bayyana nasarorin da ya samu tun bayan darewarsa kan karagar mulki a shekarar 2015, in da yake cewa, gwamnatinsa ta murkushe mayakan Boko Haram duk da cewa kungiyar kan kaddamar da hare-hare jifa-jifa a yankin arewa maso gabashin kasar. Shugaban ya kuma bayyana irin nasarar da ya samu a fannin yaki da cin hanci da rashawa. Kuna iya latsa kan hoton don sauraren cikakken shirin kan yakin neman zaben Buhari a Akwa Ibom.06/01/201910:27 -
Taron sulhunta yan siyasar Najeriya daga Tsohon Shugaban kasar
A wani taro da Tsohon Shugaban Najeriya Abdusalami Abubakar ya shirya,taron da ya hada yan siyasa da suka hada da Muhammadu Buhari shugaban kasar,wanda kuma ya sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin sa da sauran masu karawa da shi a zaben shekara mai zuwa.Wasu na bayyana cewa ba a gayyaci dan takara Atiku Abubakar a wannan taro,cikin shirin dandalin siyasa Bashir Ibrahim Idris ya samu tattaunawa da yan Najeriya.12/12/201810:00 -
Takaddama ta kaure a wasu jam'iyyun siyasar Najeriya
A cikin shirin dandalin Siyasa, Bashir Ibrahim Idris ya mayar da hankali zuwa takaddama da ta kaure a yankin arewa maso gabacin Najeriya.Datijen wannan yankin sun bukaci a goyawa daya daga cikin yan takara a zaben Shugabancin kasar baya,labarin da wasu suka musanta.Bashir Ibrahim Idris ya samu zantawa da wasu daga cikin datijen yankin a cikin shirin Dandalin siyasa daga nan Rfi.28/11/201810:00
Dandalin Siyasa
Shirin Dandalin Siyasa, yana tattaunawa tare da tafka muhawar kan al’amurran siyasa da ke faruwa a kasashen duniya, da batutuwan da suka shafi al’umma kai tsaye, wanda Bashir Ibrahim Idris ke jagoranta. Wannan Shirin na zuwa ne a karshen mako Ranar Assabar da maimaci a ranar Lahadi a Shirye Shiryen Safe da Yamma.