Ana shirin bude taron tattalin arziki a Durban
Yau ake shirin bude taron tattalin arziki duniya shiyar Afirka da za a fara a Durban da ke kasar Afirka ta kudu.
Wallafawa ranar:
Shugabanin kasashen nahiyar da ministoci da kuma masana tattalin arziki daga sassan duniya ake saran su gabatar da kasidu a wajen taron.
Najeriya ce kasa mafi karfin tattalin arziki a nahiyar, sai dai faduwar farashin mai a kasuwannin duniya ya yi mata illa tare da kasar Angola, kasa ta biyu da tafi fitar da man a Afirka.
Yanzu haka kasashen dai na ci gaba da sauya alkiblar tattalin arzikin su zuwa wasu fannoni daban da suka hada da noma da kuma hakar ma’adinai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu