Birtaniya: Cameron ya mika mulki ga Theresa May
David Cameron ya mika ragamar tafiyar da mulki ga Tharesa May wacce aka rantsar a matsayin sabuwar Firaministan Birtaniya, bayan Sarauniyar Ingila ta amince da murabus Cameron a yau Laraba.
Wallafawa ranar:
Sarauniyar Ingila Elizabeth ta biyu ta bukaci sabuwar Firaministar ta gaggauta kafa gwamnati.
Cameron ya yi murabus ne bayan rashin samun nasara a kuri’ar raba gardama da aka kada a ranar 23 ga watan Yuni kan ficewar Birtaniya a Kungiyar Tarayyar Turai.
A lokacin da ya ke jawabin ban kwana a kofar ofishin Firaminista a Downing Street a London, Cameron ya amsa fuskantar kalubale bayan shafe shekaru 6 yana Firaminista.
Cameron ya yi wa Birtaniya fatan alheri bayan ya fice Downing Street tare da iyalan shi.
Tharesa May dai ta rike Ministan cikin gida a gwamnatin David Cameron, amma babban kalubalen da ke gabanta a yanzu shi ne kare muradun Birtaniya a tattaunawar da za ta jagoranta da Tarayyar Turai kan batun ficewar kasar a Kungiyar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu