Isa ga babban shafi
Faransa

Kotu za ta fara binciken zargin ko Francois Fillon ya ba matarsa albashi

Masu shigar da kara a Faransa sun soma binciken zargin da ake yi wa dan takaran shugabancin kasar Francois Fillon na biyan makudan kudade ga matarsa da sunan ma'aikaciyar sa.

Francois Fillon dan takaran shugabancin Faransa a zaben 2017
Francois Fillon dan takaran shugabancin Faransa a zaben 2017 REUTERS/Stephane Mahe
Talla

Kafofin yada labaran Faransa sun gano cewa matarsa Penelope Fillon ba wani aiki ta yi ba da za ta sami makudan kudaden da yake biyan ta.

Ita kanta Penelope Fillon ta ki fadin  irin aikin da ta ke yi ba, wanda ake bata  makudan kudade da ake zargi.

Masu shigar da kara sun bayyana cewa za su yi bincike ne ko Francois Fillon ya yi almubazzaranci  da kudaden Gwamnati.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.