Isa ga babban shafi
Faransa

A yau ne Shugaban Faransa zai nada Firaministan kasar

Yau ake sa ran sabon shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya nada Firaministan sa da kuma kai ziyara Jamus dan ganawa da shugabar Gwamnatin kasar Angela Merkel.Shugaban ya sha alwashin hada kan al’ummar kasar wanda zaben da akayi ya rarraba.

Emmanuel Macron Shugaban kasar Faransa
Emmanuel Macron Shugaban kasar Faransa REUTERS/Alain Jocard/Pool
Talla

Macron mai shekaru 39, ya yi alkawarin ne a lokacin bikin rantsar da shi a matsayin sabon shugaban kasar ta Faransa, da ya gudana a jiya  Lahadi a birnin Paris, sati guda bayan nasarar da yayi kan Marine Le Pen, a zaben shugabancin kasar zagaye na biyu.

Daga cikin manyan batutuwan da Macron yace gwamnatinsa zata fi bai wa muhimmanci akwai sabunta tsare tsaren tafiyar da fannin tsaron kasar, yin garambawul a fannin kwadago, sai kuma jagorantar sake saita ginshikan da suka kafa kungiyar tarayyar turai EU.

Macron da ya kuma yi alwashin daukaka ‘yancin Faransawa da dimokaradiyyar kasar, ya zama shugaban kasa mafi karancin Shekaru a tarihin kasar tun bayan Napoleon Bonoparte.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.