Isa ga babban shafi
Najeriya

Birtaniya ta gargadi yunkurin juyin mulki a Najeriya

Gwamnati Birtaniya ta yi gargadi kan duk wani yunkuri na juyin mulki a Najeriya sakamakon rashin lafiyar shugaban kasar Muhamadu Buhari.

Friministan Ingila Theresa May
Friministan Ingila Theresa May
Talla

Jakadan Birtaniya a Najeriya Paul Arkwright ya ce duk wanda bai gamsu da yadda gwamnatin kasar ke gudanar da mulki ba toh ya hakura har lokacin zabe domin ya sauya ta, amma ba zasu amince da duk wani yunkuri na kifar da gwamnatin ta hanyar juyin mulki ba.

Wadanan gargadi na zuwa ne bayan wanda rundunar sojin kasar ta yi na cewar wasu 'yan siyasa na mu’amala da sojojin kasar, inda shugaban sojin Janar Tukur Buratai ya bukaci sojojin da ke sha’awar siyasa da su tube kakin su.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.