Isa ga babban shafi
Faransa

Jam'iyyar Macron za ta lashe zaben 'yan Majalisu

Wata kuri’ar jin ra’ayin jama’a ta nuna cewa, jam’iyyar shugaban Faransa Emmanuel Macron za ta iya lashe akasarin kujeru a zagayen farko na zaben ‘yan Majalisu da za a gudanar a cikin watan gobe a kasar.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron
Shugaban Faransa Emmanuel Macron REUTERS/Gonzalo Fuentes
Talla

Sakamakon sabuwar kuri’ar ta yau Talata, ya nuna cewa akwai yiwuwar jam’iyyar LREM da kawarta MoDem su samu kashi 29.5 cikin 100, yayin da ake saran Jam’iyyar Republican da kawarta su samu kashi 22.

Kuri’ar ta nuna cewa, akwai yiwuwar Jam’iyyar National Front ta samu kashi 18 kacal a kuri’un da za a kada a watan Juni.

Za a fara gudanar da zagayen farko ne na zaben a ranar 11 ga watan na Juni, yayin da za a je zagaye na biyu a ranar 18 ga watan.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.