Zaben Burtaniya
An bude rumfunar zabe a Burtaniya
'Yan kasar Burtaniya kusan miliyan 47 za su kada kuri’a yau Alhamis, domin zaben 'Yan Majalisu 650 a zaben gama gari da Firaminista Theresa May ta kira.
Wallafawa ranar:
Talla
Tuni masu kada kuri’ar wuri ta gidan waya da suka kai sama da kashi 16 suka kada kuri’un su.
Ana fafatawa ne tsakanin Jam’iyyar Conservative da ke karkashin Theresa May da kuma Jam’iyyar Labour da ke karkashin Jeremy Corbyne.
Sai dai ana hasashen ba lallai zaben ya yi armashi ba, la'akari da matsalar tsaro da kasar ke fuskanta a 'yan tsukukun nan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu