Isa ga babban shafi
Zaben Burtaniya

An bude rumfunar zabe a Burtaniya

'Yan kasar Burtaniya kusan miliyan 47 za su kada kuri’a yau Alhamis, domin zaben 'Yan Majalisu 650 a zaben gama gari da Firaminista Theresa May ta kira.

Al'ummar Burtaniya son soma kada kuri'un su
Al'ummar Burtaniya son soma kada kuri'un su REUTERS/Marko Djurica
Talla

Tuni masu kada kuri’ar wuri ta gidan waya da suka kai sama da kashi 16 suka kada kuri’un su.

Ana fafatawa ne tsakanin Jam’iyyar Conservative da ke karkashin Theresa May da kuma Jam’iyyar Labour da ke karkashin Jeremy Corbyne.

Sai dai ana hasashen ba lallai zaben ya yi armashi ba, la'akari da matsalar tsaro da kasar ke fuskanta a 'yan tsukukun nan.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.