Isa ga babban shafi
Turai

Manufofin Macron kan kwadago na samun goyon baya a Turai

Sabon shirin da shugaban Faransa Emmanuel Macron ya gabatarwa kungiyar Tarayyar Turai na kaddamar da sauye sauye a harkokinta tsakanin kasashen kungiyar ya yi nasarar tsallake matakin farko, yayin da wasu ke ci gaba da sukar shirin.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron yayin jawabin da ya gabatar a taron kungiyar Tarayyar Turai da ya gudana a Brussels
Shugaban Faransa Emmanuel Macron yayin jawabin da ya gabatar a taron kungiyar Tarayyar Turai da ya gudana a Brussels Reuters/Geoffroy Van Der Hasselt
Talla

Tuni dai ministocin kwadagon kasashen kungiyar 28 su ka bayyana goyan bayansu ga shirin musamman kan batun da ya shafi ayyukan kwadago da kuma daukar  ma’aikata.

Matukar dai shirin ya samu karbuwa tsakanin mambobin kungiyar zai bai wa kamfanoni damar tura ma’aikata wasu kasashe ba tare da biyan haraji ba, lamarin da wasu ke kallon a matsayin wata dama ta bai wa kamfanonin kofar da za su rika daukar ma’aikata daga Gabashin Turai a kudade kalilan.

A cewar ministan kwadagon Faransa, Muriel Penicaud amincewa shirin na Macron gagarumar nasara ce ga ilahirin Tarayyar Turai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.