Isa ga babban shafi
Faransa

Faransa ta kwashi rukunin farko na ‘yan ci-rani daga Afirka

Kasar Faransa ta karbi rukunin farko na bakin da ke neman rayuwa mai inganci da ta dauko daga Afirka, bayan an tan-tance su daga cibiyoyin da ta kafa a nahiyar.

Shugaba Emmanuel Macron na Faransa
Shugaba Emmanuel Macron na Faransa AFP/Ludovic Marin
Talla

Shirin da za ‘a dau tsawon shekaru ana gudanarwa na daga cikin sabon tsarin da kasar Faransa ta soma na karba bakin da suka cancanci shiga kasarta, domin rage mace-macen baki a tekun Baharum.

Wani dan kasar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, da ke cikin baki 19 da kasar ta karba, Djamal tare da matar sa da kuma yaran sa guda 4 sun sauka a tashar jiragen Charles de Gaulle bayan sun kwashe shekaru 4 a sansanin ‘yan gudun hijira.

Zalika akwai wasu 'yan kasar Sudan da suka samu mafaka a Chadi sakamakon rikicin Yankin Darfur da suma suka samu mafaka yanzu haka a Faransa.

Shirin zai bai wa baki dubu 3 ‘yan Afirka daman shiga kasar kafin shekara ta 2019, da kuma rage alkalluman mutane da ke sa rayuwarsu cikin hatsari don shiga turai ta Teku.

Duban Baki suka rasa rayukansu a kokarin tsallake tekun Baharum tun tsanartar rikicin kwararan Bakin-Haure zuwa Turai a 2015, kamar yadda kungiyar ‘yan gudun hijira ta duniya ta tabbatar.

Sai dai Sabon shirin na Faransa zai kore Bakin da basu da cancantar samun mafaka a kasar, batun da ke fuskantar suka musamman daga kungiyoyin agaji da ke bai wa Bakin matsugunai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.