Isa ga babban shafi
Faransa

Faransa ta amince da tsananta bincike a iyakoki

Majalisar ƙoli a Faransa ta bayyana amincewarta da matakan tsananta bicinke a kan iyakokin yankin Turai, abinda ke ci gaba da janyo fushi daga ƙungiyoyin da ke kare hakkin baƙin haure.

Zauren majalisar kasar Faransa.
Zauren majalisar kasar Faransa. Bertrand GUAY / AFP
Talla

Majlisar ta ce ta dauki wannan mataki ne a wani yunƙuri na yaƙi da ta’adanci a yankin Turai, ta kuma buƙaci gwamnati ta ƙara ƙaimi wajen tabbatar da dokar.

Ta kuma nuna buƙatar ganin jami’an tsaro sun mayar da hankali wajen tattance duk masu yunƙurin shiga nahiyar ta Turai.

Ƙungiyoyin da ke kare haƙƙokin yan cin-rani ne suka shigar da koke a majalisar ƙolin ƙasar, kan cewa gwamnati na amfani da ƙarfi fiye da ƙima zuwa a kan masu tafiya ci-rani, inda ta buƙaci gwamnati ta soke matakin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.