Isa ga babban shafi
Faransa

Faransa ta yi bikin tunawa da harin da ya girgiza ta

Mujahidai guda biyu ƴan asalin ƙasar Faransa, masu biyayya ga ƙungiyar al-Qaeda ne suka kai harin a shekara ta 2015, inda suka kashe ma’aikata 11 domin nuna fushinsu game da irin ba’ar da mujallar Charlie Hebdo ke yi ga batutuwa na musulunci da kuma annabi Muhammad.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ajiye furanni domin tunawa da wadanda harin Charlie Hebdo ya rutsa da su.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ajiye furanni domin tunawa da wadanda harin Charlie Hebdo ya rutsa da su. CHRISTOPHE ENA/AFP
Talla

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ajiye furanni a gaban tsohon ofishin kamfanin mujallar, a wani biki na tunawa da shekaru 3 bayan kai harin wanda ya yi sanadiyyar asarar rayuka

Harin wanda aka kai wa mujallar shi ne ya zamo kamar ɗan-ba na jerin hare-haren ta'addanci da aka kai wa ƙasar ta Faransa, waɗanda suka haifar da asarar ɗaruruwan rayuka.

Bikin wanda ya gudana a ranar Lahadi ya samu halarcin ma’aikatan mujallar ta Charlie Hebdo da jami’an gwamnati da kuma magajin garin birnin Paris Anne Hidalgo.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.