Isa ga babban shafi
Turai

Nahiyar Turai za ta fuskanci ambaliyar ruwa

Masu binciken yanayi sun yi gargadi samun mummunar ambaliyar ruwa a yankunan Turai saboda matsalolin dumamar yanayi, batun da ke zuwa kwanuki kadan da fuskantar ambaliya da kogin Seine na Paris ya haifar.

Kogin Seine  a Paris na kasar Faransa
Kogin Seine a Paris na kasar Faransa REUTERS/Gonzalo Fuentes
Talla

Ambaliyar ruwan da akayi hasashen kogunan Turai zasu haifar zai haifar da asara da dama, sama da wanda aka fuskanta a shekarar da ta gabata, sakamakon matsalolin dumamar yanayi da ke ci gaba da barazanar ga muhalli.

Hasashen da masana suka wallafa a wata mujalar yanayi na cewa, asaran da za a tafka na iya kai wa dala biliyan 19.

Rahotan ya ce alkaluman mutane da ambaliyar za ta shafa zai karu da kashi 86 cikin 100 wadda aka kiyasta a kan mutane dubu 650 a shekara.

Matsalar ambaliyar ruwa ta kasance daya daga cikin iftila’i da ke haddasa asara a Turai.

Wannan na daga cikin dalilan da ya sanya yarjejeniyar Paris na shekara ta 2015 cim-ma yarjejeniyoyin da ke ci gaba da kasancewa barazanar da haifar da dumamar yanayi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.