Isa ga babban shafi
Italiya

Dubban 'yan Italiya sun yi zanga-zangar kyama ga akidar wariya

Dubban ‘yan kasar Italiya sun gudanar da zanga-zangar nuna kyama ga akidar nuna wariyar launi a garin Macerata, inda a makon da ya gabata wani dan bindiga ya bude wuta kan bakin-haure ‘yan nahiyar Afrika.

Wasu daga cikin dubban ‘yan kasar Italiya yayin da suke zanga-zangar nuna kyama ga akidar nuna wariyar launi a garin Macerata. 10 ga watan Fabarairu, 2018.
Wasu daga cikin dubban ‘yan kasar Italiya yayin da suke zanga-zangar nuna kyama ga akidar nuna wariyar launi a garin Macerata. 10 ga watan Fabarairu, 2018. REUTERS/Yara Nardi
Talla

A bayan bayan nan dai tattaunawa kan harin da aka kai wa bakin-hauren ya mamaye yakin neman zaben ‘yan takara a kasar, wadanda zasu fafata a zaben 'yan majalisa da za’a yi a ranar 4 ga watan Maris mai zuwa.

Masu sharhi kan al'amuran siyasar Italiya na kallon batun kwararar bakin-haure cikin kasar a matsayin daya daga cikin manyan al'amuran da zasu yi tasiri a sakamakon zaben.

Sama da bakin-haure daga Arewacin Afrikca dubu 600,000 ne suka ketara takeun Mediterranean zuwa cikin Italiya a cikin shekaru 4 da suka gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.