Orban ya lashe zaben Hungary karo na uku
Jam’iyyar Firaminista Viktor Orban ta yi nasarar lashe zaben ‘yan Majalisar Dokoki da aka gudanar a jiya Lahadi a kasar Hungary, abin da zai ba shi damar ci gaba da rike mukaminsa karo na uku a jere.
Wallafawa ranar:
Bayan kirga sama da kashi 98% na kuri’aun da aka kada a zaben na jijya, jam’iyyar ta samu sama da kashi 48, yayin da sauran jam’iyyu da ke kawance da ita ke suka samu kuri’u masu tarin yawa.
Mr. Orban na matukar adawa da kara wa Kungiyar Tarayyar Turai karfi a nahiyar, yayin da ya gina yaikin neman zabensa akan tubalin kiyayyaka da karbar baki.
A yayin jawabinsa ga dandazon magoya bayansa jim kadan da lashe zaben, Mr. Orban ya ce, nasarar da suka samu za ta bai wa mutanen Hungary damar kare kansu da kasarsu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu