Jam'iyun dake kawance da gwamnatin jamus sun cimma matsaya kan bakin hare
Jam’iyyu uku da ke kawance a kasar Jamus sun amince da sabuwar alkiblar da gwamnatin Angela Merkel za ta dauka domin tsaurara matakai dangane da shigar baki a kasar.An dai share tsawon watanni bangarorin na na tattaunawa kan wannan batu, kafin cimma jituwa game da wannan shiri, da ke bayar da damar mayar da bakin da suka shiga Jamus a hannun mahukuntan kasashen da suka tsallako domin shiga kasar, yayin da a daya bangare shirin ya amince da kafa wani sansanin tattara baki a kusa da iyakar kasar da Austria.
Wallafawa ranar:
a ranar alhamis 5 ga watan yuli 2018 a lokacin da take tsakanci kan nauyin da ya rataya a wuyan gwamnatinta da suka shafi jinkai Karar a yau waziriyar jamus angela markel ta bayyana yin hannun riga ga manufar takwaranta na kasar Hongri Viktor Orban da ya ziyarci kasar ta Jamus , uwargida Markel ta ce za su kare iyakokinsu ta cikin gidan tarayyar turai ne kawai, amma ba akan manufar cewa, su rufe iyakokin gaba daya ba tamkar an rufe gida ta yadda babu wanda zai shigo
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu