Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Umar Elh Hachim kan isowar tawagar 'yan kwallon Faransa gida

Wallafawa ranar:

Dazun nan ne kungiyar kwallon kafar Faransa ta samu isowa kasar baya ga lashe kofin kwallon kafa na Duniya a Rasha a karawar da ta yi Croatia da ci 4 da 2.Jirgin da ke dauke da yan wasan ya sauka a filin tashi da saukar jirage na Roissy inda duban mutane daga sassa daban daban na kasar suka bukaci ganewa idanu bukukuwan da aka shirya a kai. Shugaban kasar da jami’an gwamnatin Faransa sun shirya tsaf domin tarben yan wasan a fadar Elysse kamar dai yadda za ku ji a tatauunawar mu da Umar Elh Hachim da ke dab da fadar Shugaban kasar Faransa.

Shugaban kasar Emmanuel Macron da jami’an gwamnatin Faransa ne su ka tarbi tawagar 'yan wasan a fadar Elysse da ke birnin Paris.
Shugaban kasar Emmanuel Macron da jami’an gwamnatin Faransa ne su ka tarbi tawagar 'yan wasan a fadar Elysse da ke birnin Paris. Eric Feferberg/Pool via Reuters
Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.