Isa ga babban shafi
Faransa

Ambaliyar ruwa ta kashe mutane a Faransa

Akalla mutane 13 sun rasa rayukansu sakamakon amabaliyar ruwa da ta afka wayankin Kudu maso Yammacin Faransa.

Yankin Aude da ya gamu da ibtila'in ambaliyar ruwa a Faransa
Yankin Aude da ya gamu da ibtila'in ambaliyar ruwa a Faransa Pascal PAVANI / AFP
Talla

Gwamnatin Yankin Aude ta ce, an samu asarar rayuka hudu ne a garin Villegailhenc, in da ambaliyar dauke da laka ta yi kamari.

Firaministan Kasar, Edouard Philippe ya bayar da jumullar alkaluman mutane 13 da suka rasa rayukansu a ibtila’in wanda ya auku a cikin daren daya gabata.

Koda yake ana fargabar cewa, ambaliyar ta yi awon gaba da wasu gawarwakin kamar yadda al’ummar yankin ke cewa.

An kuma samu tinbatsar kogi a garin Conques-sur-Orbiel, in da zurfin ruwan kogin ya karu da fiye da mita 6.

Tuni mahukuntan kasar suka bukaci jama’a da su zaune a cikin gidajensu, yayin da aka rufe makarantu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.