Isa ga babban shafi
Faransa-Macron

Macron ya yaba da sakamakon zaben tsibirin Caledonia

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya yaba da matakin yankin Caledonia na kada kuri’ar ci gaba da kasancewa karkashin Faransa a yau Lahadi.

Hoton Shugaban Faransa Emmanuel Macron yayin jawabinsa a fadar Elysee bayan fitowar sakamakon zaben raba gardamar yankin na Caledonia.
Hoton Shugaban Faransa Emmanuel Macron yayin jawabinsa a fadar Elysee bayan fitowar sakamakon zaben raba gardamar yankin na Caledonia. AFP
Talla

Cikin wasu jawabai da ya gabatar jim kadan bayan fitowar sakamakon zaben raba gardamar yankin na Caledonia, Macron ya ce abin alfahari ne ga Faransa a yau dama makomarta a gobe, kan yadda yankin ya zabi ya ci gaba da kasancewa matsayin kasa dunkulalliya tare da Faransa.

Sakamakon zaben yankin ya nuna cewa kashi 70 cikin dari na al’ummar yankin na fatan ci gaba da kasancewa karkashin Faransa, ko da dai ana ganin hakan baya rasa nasaba da euro biliyan 1 da miliyan 300, da gwamnatin ta Faransa ke baiwa tsibirin na New Caledonia duk shekara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.