Isa ga babban shafi
Faransa

Arrangamar masu zanga-zanga da 'yan sanda ta kazanta a Paris

Shugaban Faransa Emmanuel Macron zai yiwa al’ummar kasar jawabi bayan kazamar arangamar da aka samu tsakanin masu zanga-zanga da jami’an tsaro.

Yadda masu zanga-zangar adawa da karin farashin mai a Faransa suka hautsina wani yanki a birnin Paris. 24/11/2018.
Yadda masu zanga-zangar adawa da karin farashin mai a Faransa suka hautsina wani yanki a birnin Paris. 24/11/2018. REUTERS/Gonzalo Fuentes
Talla

Macron ya bayyana damuwar sa kan irin tashin hankalin da ya gani lokacin arangamar.

Zuwa yanzu dai ‘yan sandan Faransa sun jefa gurnetin barkonon tsohuwa fiye da dubu 5 kan masu riguna dorowa da suka fito zanga-zanga shekaranjiya, yayinda kuma ‘yan kwana-kwana suka kashe fiye da wutar gobara 100, a tsakanin babban filin kasar da fadar shugaban kasa, inda masu zanga-zangar suka tafka barna sosai.

Yayin wata ganawa da mukarrabansa a ofishinsa, shugaba Macron ya bayyana damuwa matuka, lokacin da suka ga irin yadda jami’an tsaro da masu zanga-zangar suka shiga juna, tamkar a fage yaki.

Kakakin shugaba Macron, Benjamin Griveaux ya ce shugaban kasar, zai gabatar da jawabi a yau, kuma tuni ya yi korafi sosai a kan yan majalisar dokokin kasa da masu fada a ji da suka kasa fito da dubaru da hanyoyin hana faruwar rikicin.

Shugabanin jam’iyyun adawa da dama ne suka nuna gowon bayansu ga masu zanga-zangar, musamman babbar abokiyar hamayyar Macron, Marine Le Pen, wadda da ta jinjina musu ganin irin yadda cikin kwana 9 suka share kasar Faransa.

A jiya Litinin kotu ta saurari a shara’o’in mutane 10 daga cikin 101 da ‘yan sanda suka kama cikin zanga-zangar, wadda ta tara mutane akalla dubu 8 a birnin Paris kadai, inda kuma mutane 31 suka samu rauni, daga cikinsu jami’an ‘yan sanda 7.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.