Isa ga babban shafi
Turai

Julian Asange ya cika sharuddan barin ofishin jakadancin Ecuado

Shugaban kasar Ecuador ya ce jagoran shafin nan mai fallasa bayanan sirri da ake kira Wikileaks Julian Assange, ya cika dukanin sharuddan da aka gindaya masa kafin barin ofishin jakadancin kasar da ke birnin London.

Julian Assange,ce jagoran shafin  Wikileaks
Julian Assange,ce jagoran shafin Wikileaks REUTERS/Peter Nicholls/Foto de archivo
Talla

Assange, mai shekaru 47 da haihuwa, ya sami mafakar siyasa a ofishin jakadancin kasar ta Ecuador da ke birnin London, tun a ranar 19 ga watan Yuni shekarar 2012, don kaucewa mika shi kasar Sweden, inda ake zargin shi da laifin yin fyade.

Assange yace ya na fargabar idan aka mika shi Sweden, daga can kuma za a iya mika shi Amurka, don a tuhume shi da laifin leken asiri.
Assange wanda dan asalin kasar Australia ne, ya share tsawon shekaru 6 boye a ofishin jakadancin kasar ta Ecuador .

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.