Isa ga babban shafi
Turai

Dubban Jama'a sun tsunduma zanga-zangar kyamar Gwamnati a Hungary

An cigaba da gudanar da zanga-zangar nuna kin jinin gwamnatin Firaminista Viktor Orban na kasar Hungary, inda dimbin masu tarzoma su ka mamaye ginin tashar talabajin na kasar da su ke zargi da mara wa firaministan baya.

Wasu daga cikin masu zanga-zanga  a kasar Hungary
Wasu daga cikin masu zanga-zanga a kasar Hungary REUTERS/Bernadett Szabo
Talla

Tarzoma ta barke ne bayan da firaministan ya yi nasarar samun goyon bayan ‘yan majalisa wajen amincewa da sabuwar dokar ayyukan kwadago a kasar, dokar da mafi yawan jama’a ke bayyanawa a matsayin bautar da jama’a.

A wata Afrilun shekarar 2018 ne Jam’iyyar Firaminista Viktor Orban ta yi nasarar lashe zaben ‘yan Majalisar dokoki da aka gudanar a kasar Hungary, abin da zai ba shi damar ci gaba da rike mukaminsa karo na uku a jere.

Mr. Orban na matukar adawa da kara wa Kungiyar Tarayyar Turai karfi a nahiyar, yayin da ya gina yakin neman zabensa akan tubalin kiyayya da karbar baki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.