Merkel ta caccaki Trump kan nuna wariyar Jinsi
Shugabar Gwamnatin Jamus Angela Merkel ta yi tir da kalaman wariyar jinsi shugaba Donald Trump akan yan Majalisun kasar guda 4, inda ta ke cewa matakin ya sabawa abinda ya daga darajar Amurka.
Wallafawa ranar:
Merkel ta nesanta kan ta daga kalaman shugaban inda ta bayyana goyan bayan ta ga Yan Majalisun.
Ita ma Firaministan Birtaniya Theresa May ta bayyana kalaman shugaba Trump a matsayin abinda ba za’a amince da shi ba, yayin da takwarar ta ta New Zealand Jacinda Arden tace ita ma bata goyan bayan kalaman.
A bangare daya kuma, 'yar Majalisa Ilham Omar ta samu gagarumar tarbo da ta koma mazabar ta, inda ta ke cewa ba za ta sauya matsayi kan sukar manufofin shugaba Donald Trump ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu