Isa ga babban shafi
Wasanni-Kwallon kafa

Tashar talabijin ta rabu da mai sharhi don kalaman wariya kan Lukaku

Wata tashar talabijin a Italiya ta ce sam ba za ta sake aiki da wani mai yi mata sharhi kan kwallon kafa ba,bayan ya furta wasu kalaman nuna wariyar launin fata kan dan wasan gaba na Inter Milan, Romelu Lukaku.

Romelu Lukaku na Inter Milan
Romelu Lukaku na Inter Milan Reuters
Talla

Da yake sharhi a tashar talabijin ta TopCalcio24, Luciano Passirani ya ce : ‘’idan ka yi fito-na- fito da shi, tabbaci hakika zai kasheka. Hanya mafi sauki ta tunkararsa ita ce kawai watakila ka ba shi ayaba goma ya ci’’.

Shugaban sashen shirye – shirye na tasahr talabijin din Fabio Ravezzani ya ce duk da Passirani ya nemi afuwa na take, tashar ba za ta sake mu’ammala da shi ba a shirye – shiryen su.

‘’Passirani dai shekarunsa 80 ne, wajen jijina wa Lukaku ya yi amfani da kalaman nuna wariya,’’ in ji Ravezzani.

"ina ganin wannan sake ne, da rashin amfani da kaifin tunani, kuma ba zan lamunci haka ba,’’ ya kara da cewa.

A wannan kaka Lukaku ya koma Inter Milan ta Italiya daga Manchester United.

Kwanan nan aka nuna wa Lukaku wariya a yayin wasan Inter da Cagliari inda ya ci wa kungiyarsa kwallo daya daga bugun daga kai sai mai tsaron raga.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.