Faransa
Mummunar gobara ta tashi a masana'antar sarrafa sinadarai
Wata mummunar gobara ta barke da safiyar yau Alhamis a wata masana’antar sarrafa sinadarai dake birnin Rouen a arewacin kasar Faransa.
Wallafawa ranar:
Talla
Babu Karin bayani kan adadin wadanda gobarar ta rutsa da su ko kuma barnar da ta tafka.
Sai dai akwai fargabar cewa, gobarar ka iya haddasa gurbacewar ruwa kogin Seine dake kusa da masana’antar.
Jami’an kwanakwana kimanin 130 suka dukufa wajen kokarin kashe gobarar, yayinda jami’an tsaro suka yiwa masana’antar kawanya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu