Isa ga babban shafi
Spain-Catalonia

Shugaba yankin Cataloniya, ya bukaci gwamnatin Spain, ta buda tattaunawa da yan aware

Dubun-dubatar masu zanga zanga ne a yau assabar 19 ga watan Okotoba 2019 ne, suka gudanar da taron gangami a birnin Barcelone na kasar Spaniya, a rana ta 5 ta soma gagarumar zanga zangar nuna rashin amincewa da hukumcin daurin da aka zartar, kan shuwagabanin yan awaren da suka yi yinkurin ballar da yankin na Kataloniya daga kasar a 2017.

Shugaban gwamnatin yankin  Catalonia, Quium Torra,
Shugaban gwamnatin yankin Catalonia, Quium Torra, EUTERS/Luis Felipe Castilleja
Talla

Tuni shugaban gwamnatin yankin na yan aware, ya yi kiran gwamnatin Spain da cewa, ba tare da gindaya sharadi ba, ta gaggauta buda shiga tattaunawa, domin magance tashe tashen hankullan da suka kazance a yankin, sakamakon hukumcin daurin gidan yari da aka zartar kan shuwagabanin na yan aware su 9.

Buraguzan duwatsu da hayakin tayyin da aka konane ya mamaye tare da kamsasa titinan Barcelona a yau assabar, bayan faruwar tashe tashen hankullan jiya juma’a da suka yi sanadiyar jikkatar mutane 180

Masu hankoron balle yankin na Katoloniya dai sun sha’ alwashin ci gaba da abinda suke yi har sai sun samu biyan bukata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.