Wani dattijo ya kai hari kan Masallaci a Faransa
Jami’an ‘yan sandan Faransa sun cafke wani dattijo mai shekaru 84 da ake zargi da kai harin bindiga tare da jikkata mutane biyu da suka haura shekaru 70 bayan sun hange shi yana kokarin cinna wuta a kofar wani Masallaci.
Wallafawa ranar:
Gwamnan Bayonne, ya ce, dan bindigan ya fara cinna wa wata mota wuta kafin daga bisani ya kama hanyar zuwa Masallacin da ke yankin kudu maso yammacin garin Bayonne .
Kawo yanzu babu cikakken bayani kan musabbabin kaddamar da wannan hari, yayin da aka bayyana mutumin a matsayin tsohon mamba a jam’iyyar masu tsattsauran ra’ayi da ke kyamar baki.
Jam’iyyar National Rally ta tabbatar cewa, maharin ya taba tsaya mata takara a shekarar 2015 a zaben yankuna kafin ta kore shi saboda wasu kalamai da ya furta da suka saba da manufofinta.
Tuni shugaban kasar, Emmanuel Macron ya yi Allah wadai da harin, kuma ya lashi takobin daukar matakin hukunta masu kai farmaki, yana mai jaddada cewa, zai kare Musulmai a kasar.
“Faransa ba za ta amince da kiyayya ba “ in ji Macron.
Harin Masallacin na zuwa ne a daidai lokacin da ake tafka zazzafar muhawara game da sanya kallabi tsakanin mata Musulmai a Faransa, dabi’ar da wasu ke adawa da ita a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu