Rasha
Jamus da Chile za su buga wasan karshe a gasar zakarun Nahiyoyi
Kasar Jamus da Chile za su buga wasan karshe a gasar cin kofin zakarun Nahiyoyi da ake gudanarwa a kasar Rasha bayan Jamus a jiya Alhamis ta ba Mexico kashi ci 4 da 1 a wasan kusa da karshe.
Wallafawa ranar:
Talla
A ranar lahadi ne za a yi fafatawar karshe domin fitar da zakara tsakanin Jamus da ta lashe kofin duniya da kuma Chile da lashe kofin gasar kasashen kudancin Amurka.
Jamus da Chile sun hadu a zagayen farko a gasar inda suka tashi 1 da 1
Kafin a buga wasan karshen za a yi karawar neman na uku tsakanin Portugal da Mexico.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu