Isa ga babban shafi
Olympics

Olympics: Los Angeles zai karbi bakuncin wasannin 2028

Birnin Los Angeles ya bayyana kudirin neman karbar bakuncin wasannin Olympics a shekarar 2028, a wani mataki da zai ba birnin Paris damar karbar bakuncin wasannin a 2024.

Magajin garin Los Angeles, Eric Garcetti
Magajin garin Los Angeles, Eric Garcetti REUTERS/Mike Blake
Talla

Paris da Los Angeles na fafatawa ne da juna kan neman karbar bakuncin wasannin Olympics a 2024 bayan kammala wasannin a 2020 da za a gudanar a Tokyo.

Yanzu birnin Los Angelses ya sauya ra’ayi daga 2024 zuwa 2028.

A ranar 13 ga watan Satumba ne hukumar wasannin Olympic za ta sanar da biranen da suka yi nasara.

Paris na son karbar bakuncin wasannin a 2024 domin ya yi daidai da shekaru 100 cur da birnin ya taba karbar bakuncin wasannin a 1924.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.