Olympics: Los Angeles zai karbi bakuncin wasannin 2028
Birnin Los Angeles ya bayyana kudirin neman karbar bakuncin wasannin Olympics a shekarar 2028, a wani mataki da zai ba birnin Paris damar karbar bakuncin wasannin a 2024.
Wallafawa ranar:
Paris da Los Angeles na fafatawa ne da juna kan neman karbar bakuncin wasannin Olympics a 2024 bayan kammala wasannin a 2020 da za a gudanar a Tokyo.
Yanzu birnin Los Angelses ya sauya ra’ayi daga 2024 zuwa 2028.
A ranar 13 ga watan Satumba ne hukumar wasannin Olympic za ta sanar da biranen da suka yi nasara.
Paris na son karbar bakuncin wasannin a 2024 domin ya yi daidai da shekaru 100 cur da birnin ya taba karbar bakuncin wasannin a 1924.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu