Isa ga babban shafi
wasanni

Najeriya za ta yi wasanni da manyan kasashen duniya

Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya Amaju Pinnick ya bayyana cewa, nan gaba tawagar Super Eagles za ta yi wasannin sada zumunta har guda biyar da manyan kasashen da suka yi fice a duniyar tamaula.

Najeriya ta doke Argetina a wasan sada zumunta a ranar 14 ga wata Nuwamba
Najeriya ta doke Argetina a wasan sada zumunta a ranar 14 ga wata Nuwamba REUTERS/Dylan Martine
Talla

Pinnick ya ce, suna shirin gudanar da wasannin ne gabanin gasar cin kofin kwallon duniya da Rasha za ta karbi bakwanci a badi.

Pinnick ya kara da cewa, sun mayar da mankali wajen ganin sun yi wasannin da kasashen da ke jan ragama a jadawalin Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya.

Sannan kuma kasashen su kasance cikin wadanda suka samu gurbi a gasar kofin duniya a Rasha.

Tuni dai Najeriya ta tuntubi wasu daga cikin kasashen don ganin cewa sun amince a yi wasannin na sada zumunta kafin zuwa Rasha a badi.

Sai dai kawo yanzu ba a bayyana sunayen kasashen ba, amma daga cikin ‘yan wasan na Najeriya akwai masu burin ganin cewa, sun yi wasa da Ingila.

Najeriya dai ta samu nasarar doke Argentina da ci 4-2 a wasan sada zumunta da suka yi a ranar 14 ga wannan wata na Nuwamba.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.