Isa ga babban shafi
Wasanni

Guardiola na ci-gaba da ba da tazara a Frimiya

Kocin Man city da ke jan ragamar teburin Frimiyar Ingila, Pep Guardiola, na ci gaba da bayyana farin cikinsa da koda David Silva wanda zura kwallayensa ya taimakawa kungiyar lalasa Swansea ci 4-0 da kuma nasara a manyan wasannin Frimiya 15.

Kocin Manchester City Pep Guardiola
Kocin Manchester City Pep Guardiola Photo: REUTERS/Fabian Bimmer
Talla

Silva ya zura kwallaye biyu, Kevin de Bruyne da Sergio Aguero kowa ya zura guda. City na da tazaran maki 11 tsakaninta da Man Utd da ke na biyu, yayin da Swansea ke karshen teburi.

Wannan shine wasa na 6 da ake doke Swansea a wasanni 9 da ta buga a gida a wannan kaka.

Yanzu dai City na da yawan kwallaye 52 a wasanni 17, inda Silva ke da 4 a wasanni 3, a karawarsu da West ham da kuma Man Utd.

Ita ma Leicester City ta samu nasaran ci 4-1 kan Southampton, a wasan da mai tsaron baya Harry Maguire ke cewa suna sake samun kwarin-guiwa da sabon kocinsu Claude Puel.

Puel dai tsohon kocin Southampton ne da ta kore shi a watan Yuni da ya gabata bayan rike kungiyar na kaka guda, da kai ta mataki da 8 a frimiya da wasan karshe na League cup.

A watan Oktoba Leicester ta dauko Puel, inda yanzu wannan shine wasa na 4 a jere da su ke yi cikin nasara.

A sauran wasannin kuma

Everton 1-0 Newcastle

Liverpool 0-0 West Brom

Man Utd 1-0 Bournemouth

Tottenham 2-0 Brighton

West Ham 1-0 Arsenal

A Bundesliga na Jamus

Hoffenheim 1-0 Stuttgart

Beyer Leverkusen 1-0 Werder Bremen

Bayern Munich 1-0 Koln

Schalke O4 3-2 Augsburg

Hertha Berlin 3-1 Hannover

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.