Isa ga babban shafi
Wasanni

"Tunusia ce kasa mafi kwarewa a fagen kwallon kafar Afrika"

Najeriya ta samu koma baya da mataki guda a jerin kasashen da suka fi kwarewa a fagen kwallon kafa.

Shugaban hukumar FIFA, Gianni Infantino.
Shugaban hukumar FIFA, Gianni Infantino. REUTERS/Rupak De Chowdhuri
Talla

Sabon sakamakon yana kunshe ne cikin rahoton da hukumar kula da kwallon kafa ta duniya FIFA ta saba fitarwa a kowane wata, wanda ta wallafa a jiya Alhamis.

Najeriya wadda a watan Janairu ke matsayin kasa ta 51 a duniya da maki 651, a yanzu ta koma kasa ta 52 a matakin kwarewa da maki 606.

Rahoton na FIFA ya bayyana kasar Tunisia a matsayin ta daya fagen kwallon kafar nahiyar Afrika, Senegal, Jamhuriyar Congo, Morocco, Masar da Kamaru sune a matakan na biyu zuwa shidda a jere, yayin da Najeriya ta ke a matsayi na bakwai.

Kasar Ghana ke biye da Najeriya a matsayi na 8, yayin da Burkina Faso da Algeria suke matsayin na tara da kuma goma.

A matakin duniya kuwa kasar Jamus ce kan gaba wajen kwarewa a kwallon kafa, biye da ita kuma Brazil da Portugal a matsayi na 2 da 3, sai kasar Argentina a matsayi na 4.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.