Bamu fidda ran lashe kofin gasar La liga ba - Zidane
Mai horar da Real Madrid Zinaden Zidane ya ce kungiyarsa bata fidda ran lashe kofin gasar La liga ba, duk da cewa abokiyar hamayyarsu Barcelona ta basu tazarar maki 15.
Wallafawa ranar:
A watan Fabarairu da ya gabata Real Madrid ta yi rashin nasara a hannun kungiyar Espanyol da 1-0, karo na farko da Espanyol ta samu nasara akan Madrid cikin sama da shekaru 10, wasan da Madrid din ke matukar bukatar lashe wa domin dada rage tazarar da ke tsakaninta da Barcelona.
A halin yanzu wasanni 12 suka ragewa kowace kungiya ta buga a gasar ta La liga, wadda mai horar da Madrid Zidane ya bayyana kwarin gwiwar zasu iya kare kofin da suke rike da shi.
A yau Asabar Madrid zata karbi bakuncin kungiyar Getafe a filin wasa nan a Santiago Bernabeu, yayin da a gobe Lahadi, Atletico Madrid zata yi tattaki zuwa filin wasan na Nou Camp domin fafatawa da kungiyar Barcelona.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu