Isa ga babban shafi
wasanni

Manchester City ta lashe kofin firimiyar Ingila

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ta lashe kofin gasar firimiyar Ingila bayan abokiyar hamayyarta, wato Manchester United ta sha kashi a hannun West Brom da ci daya mai ban haushi.

A karon farko kenan da Manhester City ke lashe kofin karkashin kocinta Pep Guardiola
A karon farko kenan da Manhester City ke lashe kofin karkashin kocinta Pep Guardiola Reuters/Jason Cairnduff
Talla

Yanzu haka Manchester City ta bai wa Manchester United wadda ke a matsayi na biyu a teburin gasar ta firimiya tazarar maki 16 duk da cewa akwai wasanni biyar da suka rage.

A karo na uku kenan da Manchester City ke lashe kofi a cikin kakanni bakwai, amma a karon farko kenan ta dauki kofin firimiyar a karkashin kocinta Pep Guardiola.

Ko da yake Guardiola ya lashe kofunan firimiya a Spain da Jamus har ma da kofuna biyu a gasar zakarun nahiyar Turai tare da Barcelona.

Manchsester City dai ta nuna bajinta a gasar firimiya ta bana, in da jefa kwallaye 93 a raga, yayin da ta sha kashi sau biyu kacal, amma Liverpool ta yi waje da ita a gasar cin kofin zakarun Turai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.