Mai yiwuwa Arteta ya maye gurbin Arsene Wenger
Bayanai sun ce mataimakin mai horar da kungiyar Manchester City, Mikel Arteta na kan gaba, a tsakanin takwarorinsa da ake fatan ganin sun karbi ragamar horar da kungiyar Arsenal.
Wallafawa ranar:
Arteta wanda tsohon dan wasan tsakiya na Arsenal ne, ya bugawa kungiyar wasanni 150, kafin daga bisani ya zama mataimakin mai horar da kungiyar Manchester City a shekarar 2016.
Har yanzu dai babu tabbacin wanda zai maye gurbin Arsene Wenger daga hukumar Arsenal, sai dai kungiyar ta jaddada kwarin gwiwar bayyana sabon mai horar da ita kafin fara gasar cin kofin duniya a ranar 14 ga watan Yuni mai zuwa.
Sauran wadanda ake dangantawa da karbar horar da kungiyar ta Arsenal sun hada da tsohon mai horar da Barcelona Luis Enrique, da kuma mai horar da Juventus Massimiliano Allegri.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu