Isa ga babban shafi
Wasanni

Ozil ba zai taka leda a gasar cin kofin duniya ba

Dan wasan gaba na Arsenal Mesut Ozil ba zai samu damar bugawa kasarsa Jamus wasan cin kofin duniya ba, bayan raunin daya samu yayin wani wasan sada zumunta da Austria ta lallasa su da ci 2 da 1 ranar asabar din da ta gabata.

Ozil dai ya samu raunin ne a karshen makon jiya, ko dai bai kwanta jinya ba amma hukumar kwallon kafar Jamus na ganin zamansa a gida zai fi amfani.
Ozil dai ya samu raunin ne a karshen makon jiya, ko dai bai kwanta jinya ba amma hukumar kwallon kafar Jamus na ganin zamansa a gida zai fi amfani. Reuters / Dylan Martinez
Talla

Haka zalika Ozil mai shekaru ba buga wasan sada zumunci da Jamus ta kara da Saudi Arabia a yau ba, wasan.

A cewar shugaban tawagar kwallon kafar ta Jamus Oliver Bierhoff dan wasan zai iya maleji ya doka wasannin cin kofin duniyar amma baya son takurawa lafiyarsa.

Ozil, wanda ya kammala kakar wasa ta bana da rauni a baya, ya yi iyakar kokarinsa wajen ganin ya shiryawa gasar cin kofin duniyar wadda za su hadu da Mexico a karon farko ranar 17 ga watan nan kafin daga bisani su fafata da Korea ta kudu da kuma Sweden wadanda dukkaninsu ke a rukunin F.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.