Isa ga babban shafi
Wasanni

Masar ta fice da gasar cin kofin duniya

Masar ta kama hanyar ficewa daga gasar cin kofin duniya bayan da mai masaukin baki Rasha ta lallasa ta da kwallaye 3-1, a wasan da suka fafata ranar Talata.

Mohamed Salah yayin zura kwallo a ragar Rasha bayan samun bugun da kai sai mai tsaron gida, a wasan da Rasha ta samu nasara da kwallaye 3-1.
Mohamed Salah yayin zura kwallo a ragar Rasha bayan samun bugun da kai sai mai tsaron gida, a wasan da Rasha ta samu nasara da kwallaye 3-1. Reuters/Henry Romero
Talla

Kwallon farko da ta shiga ragar Masar dai Kaftin din kasar ne Ahmed Fathy ya zura ta a bisa kuskure, daga bisani kuma Denis Cheryshev da kuma ArtemDzyuba suka zura guda kowannensu, lamarin da ya baiwa Rasha damar kasa ta farko, a gasar cin kofin duniya ta bana da ta fara kaiwa zagayen ragowar kasashe 16.

Masar za ta ci gaba da sa rai ne idan Saudiya ta samu nasara akan Uruguay a wasan da zasu fafata yau Laraba, zalika kuma tilas Uruguay din ta sake yin rashin nasara a wasan karshe na rukuni da za ta yi da mai masaukin baki Rasha, abinda da dama ke da ra’ayin abun da kamar wuya, wai gurguwa da auren nesa.

A bangaren Masar kuwa, kwallo daya tilo da Muhammad Salah ya jefa a bugun daga kai sai mai tsaron gida, ita ce kwallo ta farko da Masar ta ci a gasar cin kofin duniya, tun bayan shekara ta 1990.

Karo na farko kenan da Salah ya bugawa kasarsa wasa, tun bayan raunin da ya samu a kafadarsa, a dalilin ketar dan wasan Real Madrid Sergio Ramos ya yi masa a wasan karshe na gasar zakarun turai ranar 26 a watan Mayu da ya gabata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.