Isa ga babban shafi
Wasanni

Masoya na ci gaba da yi wa 'yan wasan Senegal jinjina

Masoya kwallon kafar kasashen Afrika daga sassan duniya na ci gaba da jinjina wa bajintar da ‘yan wasan Senegal suka yi, a wasan da suka samu nasara kan Poland da kwallaye 2-1, inda suke cewa ba shakka Senegal da fidda nahiyar Afrika kunya a gasar cin kofin duniyar ta bana.

'Yan wasan Senegal da magoya bayansu, yayin da suke murnar samun nasara akan  Poland a filin wasa na Spartakda ke birnin Moscow.
'Yan wasan Senegal da magoya bayansu, yayin da suke murnar samun nasara akan Poland a filin wasa na Spartakda ke birnin Moscow. Francisco Leong /AFP
Talla

Kafin wasan na ranar Talata, Senegal ce mai wakiltar nahiyar Afrika daga cikin kasashe 5, da ba a samu nasara akanta ba, a gasar cin kofin duniya da ke gudana bana a Rasha.

Da dama daga cikin magoya bayan dai sun bukaci Super Eagles na Najeriya da su yi koyi da takwarorinsu na Senegal wajen fidda magoya bayansu kunya.

A ranar Lahadi mai zuwa Senegal za ta fafata da kasar Japan, wadda ke jagorantar rukuninsu na 8 bayan lallasa Colombia da 2-1, yayinda ita kuma Poland za ta fafata da Colombia.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.