Isa ga babban shafi
wasanni

Na yi nadamar horar da Arsenal- Arsene Wenger

Tsohon mai horar da kungiyar kwallon kafa ta Arsenal Arsene Wenger ya ce, shafe tsawon shekaru 22 a wannan kungiya, shi ne babban kuskuren da ya tafka a ruyuwarsa. A cewarsa, ya yi nadamar sadaukar da komai saboda kungiyar.

Tsohon kocin Arsenal Arsene Wenger
Tsohon kocin Arsenal Arsene Wenger Reuters/Matthew Childs
Talla

Wenger mai shekaru 68 ya karbi aikin horar da Arsenal ne a cikin watan Oktoban shekarar 1996, yayin da ya raba gari da ita a karshen kakar wasannin da ta gabata.

A wata hira da jaridar Farana ta RTL, Wenger ya ce, zai tsayar da shawara kan makomarsa nan da wasu ‘yan watanni masu zuwa.

A yayin da aka tambaye shi game da babbar kuskurensa a rayuwa, sai kocin ya ce, “ watakila zama a kungiya guda har tsawon shekaru 22”

"Ni mutum ne mai son sabbin abubuwa, mai son sauye-sauye, amma duk da haka ina son fuskantar kalulabe .” in ji Wenger.

Tsohon kocin ya kara da cewa, “ Na yi nadamar sadaukar da komai saboda kungiyar domin na gano cewa, na cutar da makusantana da dama.”

“Na yi watsi da mutane da dama . Na yi watsi da iyalina” in ji Bafaranshen.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.