Isa ga babban shafi
wasanni

Monaco ta sallami kocinta saboda rashin karsashi

Kungiyar Kwallon Kafa ta Monaco da ke Faransa ta kori kocinta, Leonardo Jardim sakamakon rashin karsashin da kungiyar ke fuskanta a wannan kakar.

Leonardo Jardim
Leonardo Jardim REUTERS/Eric Gaillard
Talla

Monaco ita ce ta uku a can kasan teburin gasar Lig 1, yayin da ake ganin Thierry Henry ne zai maye gurbin Jardim don ci gaba da horar da ‘yan wasan na Monaco.

Jardim ya taimaka wa Monaco lashe gasar Lig 1 a shekarar 2017, wanda shi ne karon farko tun shekarar 2000.

Kocin ya kuma taimaka wa kungiyar wajen kaiwa matakin wasan dab da na karshe a gasar cin kofin zakarun Turai ta shekarar 2016-2017.

Kazalika ya taimaka wa wajen gina ‘yan wasa irinsu Kylian Mbappe da yanzu haka ke taka leda a PSG.

A shekarar 2014 ne Monaco ta kulla kwantiragi da Jardim mai shekaru 44.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.