Wasanni
Robben zai kawo karshen zamansa a Bayern Munich
Arjen Robben ya bada tabbacin cewa zai rabu da kungiyarsa ta Bayern Munich a watan Juni mai zuwa, lokacin da yarjejeniyarsa za ta kare.
Wallafawa ranar:
Talla
Robben wanda zai cika shekaru 35 a watan Janairu mai zuwa, ya samu damar bugawa Bayern Munich wasanni biyu ba, saboda raunin da ya samu a cinya, wanda ya warke a yanzu.
Dan wasan zai samu damar bugawa kungiyar tasa wasan gasar zakarun turai na ranar Laraba da za su yi tattaki domin fafatawa da Ajax a birnin Amsterdam.
Robben tsohon dan wasan kasarsa ta Holland ya soma bugawa Munich kwallo a shekarar 2009.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu