Isa ga babban shafi
Wasanni

Portugal za ta kwace lambar yabo mafi girma da ta baiwa Ronaldo

Shugaban Portugal Marcelo Rebelo de Sousa, ya ce gwamnatinsa tana nazari kan yiwuwar kwace babbar lambar yabo da ta baiwa dan wasan kasar Cristiano Ronaldo.

Cristiano Ronaldo, yayin wasan kusa da na karshe da suka fafata da Wales, a gasar cin kofin kasashen nahiyar Turai na shekarar 2016.
Cristiano Ronaldo, yayin wasan kusa da na karshe da suka fafata da Wales, a gasar cin kofin kasashen nahiyar Turai na shekarar 2016. REUTERS/Kai Pfaffenbach Livepic
Talla

Matakin a cewar shugaba Rebelo de Sousa, na da nasaba da hukuncin biyan tara da kotun Spain ta yanke kan Ronaldo, bayan samunsa da laifin kin biyan haraji, yayin da yake wasa a kungiyar Real Madrid.

A shekarar 2016 Portugal ta karrama Ronaldo da lambar yabo mafi girma da ake baiwa farar hula ta ‘Portuguese Order of Merit’ a turance, bayan taimakawa kasar da ya yi, wajen lashe gasar cin kofin kasashen nahiyar Turai.

Sai dai a ranar Talatar da ta gabata, wata kotun Spain ta yanke hukuncin tilasatawa Cristiano Ronaldo biyan Dala miliyan 3 da dubu 57 saboda kin biyan makudan kudade na haraji ga gwamnatin kasar.

Da fari hukuncin kan Ronoldo na daurin shekaru 2 biyu ne a gidan Yari amma aka sassauta hukuncin zuwa biyan tarar euro dubu 365 na take, tare da biyan karin euro miliyan 3 da dubu 200.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.