Barcelona da Liverpool sun yi nasarar zuwa mataki na gaba a gasar Zakarun Turai
A ci gaba da gasar neman kofin zakarun Turai, an samu karin kungiyoyi biyu da suka wuce zuwa zagayen Quarter-Final bayan da suka yi nasara a wasannin da suka buga cikin daren laraba, wato Liverpool da kuma Barcelona.
Wallafawa ranar:
Liverpool ta yi nasara a gidan Bayern Munich 3-1 a filin wasa 3-1 na Alianz Arena, abin da ya bai wa Liverpool damar shiga sahun kungiyoyi 8 sau biyu kenan a jere.
Dan wasan Liverpool Sadio Mane ya zura kwallayen biyu a wasan, yayin da Van Dijk ya yi nasarar zura kwallo daya.
Wannan dai ba karamar nasaba ba ce ga ‘yan wasan kasar Ingila, domin kuwa daga cikin kungiyoyin kwallo kafa 8 da suka rage a gasar ta zakarun Turai, 4 sun fito ne daga kasar.
Wannan ne dai karon farko da za a shiga zangon kungiyoyi 8 ba tare da Bayern Munich ba, tun bayan da ta fuskanci irin wannan koma-baya a kakar wasannin 2011 lokacin da ta sha kashi a hannun Inter Milan ta Italia.
Barcelona ta lallasa Lyon
A cikin daren laraba, an fafata tsakanin Barcelona da Lyon, inda aka tashin wasan Barcelona ce ke da nasara 5-1, kuma Lionel Messi ne ya zura kwallaye biyu.
To sai dai an dan samu cece-kuce sakamakon wani bugun fenirati da aka bai wa Barcelona a wasan na jiya, domin sai da aka yi amfani da kemarar taimaka wa alkali kafin tabbatar da hakan a minti na 16 da fara wannan wasa.
A zagayen farkon dai an tashi tanjaras ne ba tare da wani ya zura kwallo a raga ba tsakanin Lyon da kuma Barcelona.
A yanzu dai kungiyoyin da suka yi saura a gasar ta Zakarun Turai sun hada da Barcelona, Liverpool, Manchester City, Tottenham, Manchester United, Juventus, Ajax da kuma Porto, kuma a gobe juma’a ne hukumar kwallon kafar Turai za ta fitar da jadawali dangane da yadda wadannan kungiyoyi za su kara a matakin Quarter Final
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu