Isa ga babban shafi
Wasanni

Libya ta lallasa Najeriya a wasan neman tikitin zuwa gasar Olympics

Libya ta lallasa Najeriya da kwallaye 2-0 a zagayen farko na wasan kwallon kafa da suka fafata, na neman cancantar halartar gasar Olympics da kasar Japan za ta karbi bakunci.

Najeriya na fuskantar barazanar rasa damar halartar gasar Olympics a bangaren kwallon kafa.
Najeriya na fuskantar barazanar rasa damar halartar gasar Olympics a bangaren kwallon kafa. REUTERS/Nigel Roddis
Talla

A ranar Litinin mai zuwa, kasashen za su sake fafatawa a zagaye na 2, inda najeriya za ta karbi bakuncin Libyan a babban filin wasan jihar Delta da ke Asaba.

Hukumar lura da wasannin Olympics, ta takaita wasannin kwallon kafa neman cancantar halartar gasar ce a tsakanin ‘yan wasan da ke kasa da shekaru 23.

Sauran wasannin neman cancantar da aka buga a ranar Laraba 20 ga watan Maris, 2019, tsakanin kasashen nahiyar Afrika sun kunshi, wasan da Jamhuriyar Dimokaradiyar Congo, ta lallasa Morocco da 2-0 a birnin Kinshasa.

Sudan ma lallasa Kenya ta yi da kwallaye 2-0 a birnin Omdurman, yayinda Guinea ta samu nasara kan Senegal da  2-1.

Zambia tayi tattaki zuwa Malawi ta kuma samu nasara da 1-0.

Wasa tsakanin Burundi da Congo Brazzaville da aka fafata a birnin Bujumbura kuwa an tashi 0-0.

Kasashe uku ne za su wakilci Nahiyar Afrika a fagen kwallon kafa, yayin gasar ta Olympics za ta gudana a Tokyo babban birnin kasar Japan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.