Libya ta lallasa Najeriya a wasan neman tikitin zuwa gasar Olympics
Libya ta lallasa Najeriya da kwallaye 2-0 a zagayen farko na wasan kwallon kafa da suka fafata, na neman cancantar halartar gasar Olympics da kasar Japan za ta karbi bakunci.
Wallafawa ranar:
A ranar Litinin mai zuwa, kasashen za su sake fafatawa a zagaye na 2, inda najeriya za ta karbi bakuncin Libyan a babban filin wasan jihar Delta da ke Asaba.
Hukumar lura da wasannin Olympics, ta takaita wasannin kwallon kafa neman cancantar halartar gasar ce a tsakanin ‘yan wasan da ke kasa da shekaru 23.
Sauran wasannin neman cancantar da aka buga a ranar Laraba 20 ga watan Maris, 2019, tsakanin kasashen nahiyar Afrika sun kunshi, wasan da Jamhuriyar Dimokaradiyar Congo, ta lallasa Morocco da 2-0 a birnin Kinshasa.
Sudan ma lallasa Kenya ta yi da kwallaye 2-0 a birnin Omdurman, yayinda Guinea ta samu nasara kan Senegal da 2-1.
Zambia tayi tattaki zuwa Malawi ta kuma samu nasara da 1-0.
Wasa tsakanin Burundi da Congo Brazzaville da aka fafata a birnin Bujumbura kuwa an tashi 0-0.
Kasashe uku ne za su wakilci Nahiyar Afrika a fagen kwallon kafa, yayin gasar ta Olympics za ta gudana a Tokyo babban birnin kasar Japan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu