Isa ga babban shafi
wasanni

Arsenal ta kado Tottenham daga teburin firimiya

Kungiyar Kwallon Kafa ta Arsenal ta doke Newcastle a Emirates da ci 2-0, nasarar da ta ba ta damar darewa saman Manchester United da Tottenham a teburin gasar firimiyar Ingila, in da a yanzu take a matsayi na uku biye da Liverpool da Manchester City da ke matsayi na daya da na biyu.

Kocin Arsenal, Unai Emery ya jinjina wa Mesut Ozil kan rawar da ya taka a wasansu da Newcastle a Emirates
Kocin Arsenal, Unai Emery ya jinjina wa Mesut Ozil kan rawar da ya taka a wasansu da Newcastle a Emirates Reuters / Dylan Martinez
Talla

Aaron Ramsey ne ya fara ci wa Arsenal kwallonta ta farko a minti na 30, kafin Alexandre Lacazette ya kara ta biyu a minti na 83.

A farkon watan Fabairun da ya gabata, Tottenham ta bai wa Arsenal tazarar maki 10 a teburin gasar, amma wannan nasarar da ta samu akan Newcastle ta sa a yanzu, Arsenal din ta kere wa Tottenham da Manchester United da maki 2.

Arsenal na da maki 63, yayinda Tottenham da Manchester United kowacce ke da maki 61.

A karo na 10 kenan a jere da juna da Arsenal ke samun nasara a wasannin da ta yi a gidanta na Emirate a gasar Lig, kuma raban da ta nuna irin wannan bajintar tun a watan Disamban 1997 da kuma watan Mayun 1998.

Kungiyar ta kama hanyar nemawa kanta gurbi a gasar zakarun nahiyar Turai bayan ta shafe shekaru biyu ba tare da samun tikitin halartar babbar gasar a Turai ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.