Isa ga babban shafi
Wasanni

Ba zan sha maganin da zai rage karfina ba - Semenya

Shahararriyar ‘yar tseren gudu ta kasar Afrika ta Kudu, Caster Semenya, ta kafe kan matsayinta na kin amincewa da bukatar shan magunguna da za su rage tsabar karfi da zubin da take da shi tamkar namiji.

Caster Semenya, shahararriyar 'yar tseren gudu daga Afrika ta Kudu.
Caster Semenya, shahararriyar 'yar tseren gudu daga Afrika ta Kudu. REUTERS
Talla

A watannin da suka gabata Semenya ta garzaya kotu domin, tilastawa hukumar shirya wasannin motsa jiki ta duniya, ba ta damar ci gaba da fafatawa a wasannin motsa jiki da hallitarta, ba tare da rage mata karfi, ko dora ta kan magungunan da za su rage kirar karfi ta namiji da take da shi ba.

Gasar karshe da Semenya ta lashe, ita ce ta gudun mita 800 a babban birnin Qatar, wato Doha, inda ta kammala gudun mita 800 din cikin minti daya, da dakika 54.

Yayin gasar dai Semenya ta baiwa Francine Niyonsaba, da ke biye da ita a matsayin ta biyu, tazarar mitoci 20, saboda karfin gudun da take da shi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.