Isa ga babban shafi
Wasanni

Real Madrid za ta yi tankade da rairaya

Rahotanni daga Spain sun ce akwai yiwuwar Real Madrid za ta saida ‘yan wasanta da dama bayan kammala karkare kakar wasa ta bana.

Kocin kungiyar Real Madrid Zinedine Zidane.
Kocin kungiyar Real Madrid Zinedine Zidane. © REUTERS/Susana Vera
Talla

Matakin ya zo ne a dai dai lokacin da kocin kungiyar Zinaden Zidane ke shirin aiwatar da yin gagarumin garambawul ga kungiyar, domin maido da karsashin da ta rasa a baya.

‘Yan wasan da ake sa ran Real Madrid za ta saida sun hada da Gareth Bale, James Rodriguez wanda ke zaman aro a Bayern Munich, Jesus Vallejo, Mateo Kovacic, Dani Ceballos, Marcos llorente da kuma Lucas Vazquez.

Sauran yan wasan kuma sun kunshi mai tsaron ragar kungiyar ta Real Madrid Keylor Navas, Brahim Diaz Mariano Diaz sai kuma Oscar Rodriguez.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.